Wasanni - Yadda NFF ta rarrashi Isma'ila Mabo bayan ta mace shi

Share:

Wasanni

Miscellaneous


Shirin Duniyar Wasanni tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kacokan da tsohon kocin tawagar mata ta Najeriya, Isma'ila Mabo wanda Hukumar Kwallon Kafar kasar ta NFF ta rarrashe shi tare da ba shi hakuri bayan ta ki gayyatar shi  zuwa wani biki da ta shirya domin karramar tsoffin 'yan wasan mata da ya horas da aka gudanar a birnin Lagos.