News
Shirin 'Lafiya Jari Ce' na wannan mako tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan yadda majinyata daga Najeriya musamman masu rike da madafun iko kan tsallake asibitocin cikin kasar tare da balaguro wasu kasashen don duba lafiyarsu, lamarin ake dangantawa da sake tabarbarewar harkokin kula da lafiya a ilahirin asibitocin gwamnatin kasar.